Tuesday, 7 November 2017

KO KUN SAN MUHIMMANCIN MATA KUWA?



ILIMI DA MUHIMMANCINSA GA MATA
Kafin zuwan wayewar kai da ilimi, mata basu da fada  aji cikin al’umma. An dauki mata ba a bakin komi ba face masu dawainiyar gida da kula da ‘yara. A zamanin jahiliyyah a kasar Saudiya birne ‘ya’ya mata akeyi da ransu, mata basu da gado, an dauke su kamar rigar da ake canzawa ko wane lokaci aka ga dama.
Karatun ‘ya mace ba karamar fa’ida yake da shi al’umma ba. Sabili da mahaifiya ita ke tare da yara kullum a gida, ilimin zai sa kanta ya waye ta san muhimmancin karatu, zuwa asibiti, bawa yaranta tarbiyyah ta kwarai ta inda har zasu zama masu kishin kasa. Mace me ilimi zata taimaka wurin bawa mijinta shawarwari masu amfani da zasu taimaka wurin gudanar da harkokin yau da kullum.
Har ila yau, yara mata dake karkara ana tauye musu hakkin su na rashin samun ingantaccen ilimi ta hanyar aurar dasu tun a shekarun da basu wuce kirgen dangi ba. Wala Allah in tasami miji me kishin karatu yasakata, wala Allah kuma ta qare da jinyar yoyon fitsari bayan mijin ya mata sakin wulakanci.  Ba addinin da ya hana neman ilimi a duniya. Annabi Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yace  neman ilimi wajibi ne akan kowane Musulmi, Tirmidhi ne ya ruwaito shi lamba ta saba’in da hudu.
Shawarar da zan bawa gwamnati shine, a saka dokar dole sai yarinya ta kai shekaru sha shida kafin a aurar da ita. Akalla kafin nan ta kara sanin ciwon kanta, ta gama karamin mataki na  makarantar gaba da firamari da kuma ilimin yin ginshiqan musulunci ba tare da ta kwafsa ba. A kuma saka taran duk mahaifi koh marikin yarinyar da ya aurar da ita kafin shekarun da aka kayyade  koh ya hana ta zuwa makaranta ya biya kudi masu yawan gaske koh zaman gidan maza na shekaru adadin kudin.
A lokutan baya, ba a  baiwa ilimi muhimmanci ba kuma ba a damu a ba ‘ya mace ilimin addini ba ballantana na zamani. Har ana cewa “Sabbi saukar Mata”. Watau da sun kai Suratul Sabbi shi ke nan sun bar karatu da neman ilimi. Suratul Sabbi kuwa ita ce Surah ta 97 a Alkur ‘ani, kuma ita ce Izifi na daya daga cikin Izifi Shittin na Alkur’ani.

Mace a wancan zamanin, idan ta kai shekara 14 ko 15 sai a yi mata aure. Hakan yana da kyau kamar yadda addinin ya nuna. Yin aure bai kamata ya hana ilimin mata ba amma. Abin takaicin sai a bar su a gida ba su san yadda ake tsarki ba.
Daga baya da ilimin boko ya fara shigowa kasashen Hausa, sai aka dauki karatun Boko a matsayin wani abu marar amfani. Ba a ba ’ya’ya maza da mata damar su yi karatun ba. Bayan an fara gane muhimmancin karatun boko ne, aka fara ba maza damar yin karatun sosai.
A manyan makarantun boko akwai sashi daban-daban, wadanda dalibi zai iya yin karatu. Akwai kamar Likitanci da karatun zama Injiniya da na harsuna irinsu Turanci da sauransu. A bangaren karatun likitanci da Unguwarzoma, wadannan sashi ne da mata za su fi mayar da hankali, domin hakan zai amfani al’umma. A wasu asibitocin, maza ne wadanda ba muharramai ba ke duba mata. To a maimakon haka, zai fi kyau a ce mace ta duba ’yar uwarta.
Mafi yawancin tsokacin mutane a kan karatun ’ya’ya mata a kan yanayin makarantun ne. Yadda ake hada maza da mata, yadda tsarin sanya tufafi yake da sauransu. Idan har gwamnati na so ta habaka ilimin mata a Najeriya, musamman a arewa, ya zama dole ta yi la’akari da halayya da addini da zamantakewa da kuma al’adun mutane wajen tsara makarantu da kuma yadda ake karatun, haka zai taimaka wajen bunkasa ilimi sosai a Arewacin Najeriya.
Ina so mata su sani neman ilimi wajibi ne, sai dai su sani ya zama dole su tsare kansu daga aikata dukkan ayyuka marasa kyawu, iyaye su sanya idanu wajen lura da yadda ’ya’yansu mata suke karatu.


Abubuwa 4 da ke iya zama cikas ga ilimin 'ya mace a Arewacin Najeriya
Ga abubuwan 4 wanda sune nake ganin zasu iya zama cikas ga ilimin ‘ya mace a Arewacin Najeriya:

 Talauci: Game da bincike, kashi 28 cikin 100 sunyi imanin cewa talauci ne babban cikas ga ilimin diya mace a Najeriya. A Arewacin Najeriya kuwa, ko shakka babu shine babban abunda yake kawo cikas. Talauci ne ke sanya iyaye na aika yaransu mata talla wanda ke hanasu zuwa makaranta.
Al’ada: A Arewacin Najeriya, al’adarmu tayi babban tasiri akanmu. Wanda ya shafi cigabanmu da kuma wayewarmu. Duk da cewa anyi ittifakin cewa ilimantar da diya mace nada muhimmanci ga al’umma, har ila yau akwai iyaye wadanda suke hana yaransu mata karatu. Game da cewar wasu, ai aikin mace shine kula da gida. Duk da cewa addinin musulunci ya wajabta neman ilimi da ilimantar da iyali da yara, wannan kalubale bai gushe a Arewa ba. Rashin sani a bangaren iyaye: Bincike ya nuna cewa kaso 18 cikin100 sun amince da cewa jahilcin iyaye babban kalubale ne. kashi 25 sunyi imanin cewa idan aka ilimantar da iyayen, zasu fahimici muhimmancin ilimantar da ‘ya mace. Wani sakamakon rashin ilimi a bangaren iyaye shine, a tunaninsu idan ‘ya mace tayi karatu, ba zata amfanesu da shi ba, illa mijinta da yaranta. Saboda haka, sai su mayar da hankali wajen ilimantar da yara maza.
Saurin aure: Kashi 15 na mutane sun yi imanin cewa babban kalubalen da ke zama cikas ga ilimin ‘ya mace shine aurar da su da akeyi da wuri. A wasu wurare a Arewa, ana aurar da yara mata kafin su san ciwon kansu. Kana kuma ana aurar da su ga jahilan mazaje wadanda ba zasu ilimantar da su bayan aurensu ba. wannan sai ya haifar da zuriya jahila.

Nuna jinjinarka zuwa ga marubucin ta hanyar danna maballin like ko kuma ka bada taka gudunmuwa ta hanyar yin commenting da naka ra'ayi dan nuna gamsuwa zuwa ga marubucin. Yin hakan zai kara masa kwarin guiwa.


© Muhammad Sunusi Nalado
+2347030339117
Shafin Bahaushen Arewa


Labels: ,

Wayar Salula:Zuma ga Zaki ga Harbi




A wannan zamani da muke, idan ka duba a cikin al’ummar mu, waya ta zama ruwan dare a tsakanin kananan yara da matsan mu, ganin haka ne ma yasa marubucin yayi nazari game da irin illar da waya take yi ga matasa da kananan yara.
Ita Kalmar karamin yaro a kundin tsari tana nufin yaro ko yarinya wanda bai haura shekaru 18 ba (a takaice wanda bai balaga ba) dalili kuwa shine a bincike na masana sun yi amanna da cewa sai mutum ya kai shekara 18 ne ya soma mallakar hankalinsa, a wannan shekaru ne dokar kasa ta hau kan shi.
To a hakikanin gaskiya, duk abu wanda aka kirkira, yanada alfanu, haka zalika yana da illoli tari duk da cewa shi Alexander Graham Bell (wanda ya kirkiri wayar tarho) bai da makusa, yayi amfani da hikimarsa ne wurin bada tasa gudunmuwa dan cigaban dan Adam a rayuwa duk da cewa an samu wasu sauye-sauye bayan tashi fasahar. Ban sani ba ko akwai wata doka da ta hana matasa ‘yan kasa shekara da 18 amfani da wayar salula ba, saboda har yanzu akan bincike nake dan gani ko zan samu. Kididdiga ta nuna cewar kaso 78% a cikin 100% na yara dake tsakanin shekara 12-17 sun riga sun mallaki wayar salula. Amfani da wayar salula da matasa ‘yan kasa da shekara 18 ke yi ya zama barazana ba ma akan su kawai ba, a’a har ma ga al’umma duka.
A nan marubucin ya iyakance kansa ga illolin wayar salula a hannun matasa da kananan. Kafin mu tattauna illolin, ga wasu daga cikin amfaninta/muhaimancinta:
    

  •   Zumunci: Waya ta taimaka sosai wurin sada zumunci. Sada zumunci ta hanyar hada ‘yanuwa wanda suke nesa da juna.
  • Kasuwanci: Waya tana taimakawa wurin gudanar da harkokin kasuwanci. Manyan ‘yan kasuwa da ma kanana suna amfani da waya sosai domin gudanar da harkokin kasuwancin su, a yau mai son siyan kaya a wurin wani dan kasuwa zai iya daga wayarsa daga gida ya kira abokan cinikin sa dan siya ko siyar da hajarsa a nan  gida Najeriya ko a kasar waje.
  • Agajin gaugawa: Wayar salula ta taka muhimmiyar rawa wurin sadarda agaji na gaugawa. Misalin maras lafiya zai iya amfani da wayarsa dan kiran wani dan’uwan nasa ko kuma ya kira likita domin dauki a gareshi.
To wannan kadan kenan daga cikin alfanu na wayar salula, wanda zai iya kasancewa manya har matasan suna amfanuwa da shi. Amma illolin wayar salula gasu zan zayyano a kasa; 

Lalacewar tarbiyya: Saboda samun cigaba na zamani da ya auku, kamar yadda aka ambata a baya, wayar salula tayi jagora sosai da gaske wurin wargaza tarbiyyar matasa. Idan kayi duba ga yanar gizo gizo, akwai manhjoji da suke basu da aiki wanda ya wuce zuba hotuna da bidio na kallo wanda suke kunshe da batsa da nuna tsiraici. A bincike na masana da aka gudanar kwana-kwanan nan ya nuna cewar akwai irin wadannan manhajoji akan yanar gizo sama da dubu dari. Haka binciken ya nuna cewa, Najeriya tana daya daga cikin kasashe wanda sukafi kowa shiga wannan shafuffuka, wannan abun iyaye su duba ne, su saka ido akan ‘yan ‘yansu domin ganin sun kubutar da su daga irin shafuffukan, dalili kuwa shine kowa ya sani a addinnace walau Krista ko Musulmi cewa bayyanar da tsiraici bai karbuwa ga al’ummar mu domin yana taimakawa wurin rugejewar tarbiyya da samun barna ta bangaren fyade, haka ma yana ruguza al’umma da imaninsu. Akwai abunda ake kira da ‘cybersex’ a turance, ma’anarsa shine zina ta yanar gizo ko shafukan sada zumunta wanda hakan yana faruwa ba tare da sanin iyaye ba. Yana faruwa ta hanyar kiran waya ko kuma zance a shafukan sada zumunta. Masu wannan dabi’a suna bin hanyar taba al’aurar su dan su biyawa kansu bukata. Wannan ba karamin fasadi bane garesu da kuma al’umma baki daya.

Haduwa da abokai bata gari: A nan Kalmar aboki bata gari yana nufin aboki wanda yake neman wanda zasu yi tarayya da shi wurin wata harka ta barna. Daga gida ko a wani wuri, wani saurayi zai iya hada lambobi a wayarsa ya danna kira, burinsa ya samu mace ta daga wayar. Idan yayi nasa kuwa ya samu macen ta dauka sai ya gabatar da manufofinsa, idan itama ra’ayinta yayi daidai da nasa shikenan sai barna ta auku. Idan kuwa yayi rashin nasara aka samu akasin bata karbi ra’ayin nasa ba, sai yayi kokarin jawo hankalinta da kalamai har ta dawo ta amince da zancensa saboda karancin wayo.
    
     Tabarbarewar Karatu: Binciken masan ya nuna cewar yawan amfani da da wayar salula da matasa keyi yana haifar da koma baya ga iliminsu. Wannan ne ma yasa makarantu da dama suka hana dalibansu mu’amula da wayar salula yayinda suke cikin farfajiyar makaranta. Daliln haka kuwa abune mai saukin fahimta. A wannan zamani da muke ciki ya sanya bincike yayi karanci a tsakanin matasanmu ta hanyar yin amfani da shafin ‘Matambayi Baka Bata’ wato GOOGLE turance. Yana taimakawa wurin satar amsa matuka. Shi wannan shafin yasa matasanmu sun manta amfanin dakunan karatu wato ‘Library’. Sannan kuma ita wannan salular tana kunshe da na’urar lissafi da na’urar daukar hoto, duka wannan suna taimakawa wurin dauke hankali a lokacin darasi.
    
     Cãca: Shafuka da ake ta kirkirowa a yanzu dangin cãca sun zama ruwan dare. Misalin irin su akwai ‘9jabet, NairaBet, 365bet’ sun taimaka kwarai wurin afkawar matasanmu da yara kanana cikin halaka domin shafin yana bada dama da duk wanda ya shiga yayi zabi tsakanin kungiyoyin kwallon kafa wadda za tayi nasara akan wata ta hanyar sadaukar da wasu kudade.
  
     Rashin Isasshen Barci: Hakika barci yana da matukar amfani ga matashi. A kowacce rana matashi yana bukatar yayi barci na awa 9 da rabi to amma wasu basu amfani da wannan damar dan ganin sun cimma wanna awowin suna barcin sai dai su mayar da hankalinsu ga yanar gizo ko shafukan sada zumunta irin su Facebook ko Whatsapp. Zaka ga matashi ya kwashe lokaci mai tsawo yana rike da wayarsa, ya hana idanunsa runtsawa  a karshe sai kaga yaro idan yaje aji wurin darasi ka sameshi yana barci wannan illar ta jawo koma baya ta hanyar neman ilimi.

        Sirri: A wannan zamani da muke ciki yanzu, zamani ne wanda sirrin mu gaba daya bamu da tabbacin sa kuma yana kara kasancewa cikin barazan idan muka barshi a fili ta hanyar da makiya zasu iya amfani da shi wurin zambatarmu da wannan damar. Abun mamaki ne ga yanda wani bincike ya nuna cewar kashi 52 na matasa basu kashe na’urar GPS da ke a cikin salularsu idan suna amfani da yanar gizo ko shafukan sada zumunta. Wasu har sun kai matsayin da suna yada adireshin su a shafukan sada zumunta, daukar hotuna a gidajen su suna aikawa kai har ma hada lokaci na sirri dan saduwa ta fuska da wani wanda basu taba gani ba a zahiri sai dai fira a yanar gizo. Wannan bai tsaya nan ba, wasu sun kai matsayin suna bayyana zuri’arsu ko rayuwarsu wadda ta shafesu ga abokai da ko wani bako a shafukan sada zumunta.  Ni da kaina nayi badda kama nayi fira da wata karamar yarinya, abubuwanda ta fada mun game da rayuwarta ya gigita ni, har ta kai tana fada mun sirrikanta na boye. Wannan abu ne mai matukar tsoratarwa.


Iyaye sun bijiro da dalilai daban-daban  da yasa suke so ‘ya’yansu su mallaki wayar salula. Ya kamata ayi nazari mai zurfin gaske tsakanin amfaninta da kuma illolinta kafin a basu damar rika wannan na’ura. Wani mai bincike ya saki bidiyo na kallo inda ya nuna yanda yake magana da matasa a asirce ta shafukan sada zumunta kai har ma hada wata haduwa ta musamman a wani kebantaccen wuri. Yayi hakan ne tare da sanin iyayen su  dan ya nusar da su iyayen illar wayar salula. Zaka iya kaddara yanda karshen labarin ya kasance idan ace wani mutum ne wanda ba’a san asalin sa.

Balaga, kaifin tunani da kalar wayar dake hannun matasa da makamantansu, sune ya kamata a duba kafin a baiwa wani matashi damar rike waya. Haka zalika, tsauraran matakai na bukatuwa wurin kula da hanyoyi da yara suke mu’amula da waya. 
Kar ka manta ka danna maballin like dan nuna jijinawarka ga marubucin. Bugu da kari ma, zaka iya bata taka gudunmuwa ta hanyar yin comment dan nuna jin dadinka. Yin hakan zai kara kwarin guiwa ga marubucin.
© Muhammad Sunusi Nalado
+2347030339117
Sahfin Bahaushen Arewa
2017.

Labels: ,

Thursday, 19 October 2017

Kungiyoyin Matasa.

Matasa! Shin ko kun san kuna da muhimmiyar rawa wadda zaku iya takawa a yankunanku?

Duba da yanda halinda ilimi yake a ciki a kasar mu musamman nan gida Arewa, yasa nayi wannan rubutu domin fadakarwa ga matasan mu da tunatar da su muhimmacin ilimi da kuma rawar da zasu iya takawa wajen karfafawa na kasa dasu dan cigaban mu.

Ilimantarwa da tarbiyya al’amura ne masu girman matsayi da daukaka kuma sune ginshikin rayuwa da suke kai mutum ga kyakkyawar rayuwa da samun cikan kamala. Hakika mutum wani halitta ne da ke bukatar tarbiyya a fagen rayuwarsa kuma sakamakon kyakkyawar tarbiyya  zai iya kai wa ga babban matsayi na tsarkakan ruhi da yalwan ilimi a rayuwarsa ta duniya. Hakika tun daga yarantar mutum har zuwa girmansa da kuma zuwa karshen rayuwarsa yana rayuwa ce a kan matakai masu bibiyar juna kuma a tsawon matakan rayuwarsa yana da damar kai wa ga mataki madaukaki, kamala da cika.

Hakika matakin kula da tarbiyyar yara lamari ne mai muhimmanci da ke bukatar sanya ido da lura, kuma dole ne a kan mahaifa ko masu kula da tarbiyyar yara su kasance masu cikakken sa- ido kan tarbiyyar yaran da lura da dabi’unsu. A fili yake cewa tarbiyya da ilimantarwa al’amura ne masu muhimmanci da daukaka a rayuwar mutum musamman daga lokacin yaranta zuwa lokacin samartaka, kuma wadannan matakai biyu na yaranta da samartaka suna kunshe da tarin matsaloli na musamman, sakamakon haka tarbiyya da ilimantarwa suna da matakai, kuma kowane mataki yana da nashi matsayi da muhimmanci na musamman.
Tarbiyya a ma’anarta ta lugga tana nufin karuwa, girma da habaka a kan tafarkin da ake bukata, ko kan tafarki mai kima. Yayin da neman ilimi hanya ce da take kai mutum ga samun tarbiyya da kyakkyawan sakamakon rayuwa. Don haka a fili yake cewa neman ilimi da samun tarbiyya sune shimfida kuma ginshikai da suke kai ga inganta rayuwar bil-Adama tare da taimaka masa wajen cimma burin rayuwarsa na kai wa ga matsayin cika da kamala da ake bukata.

Akwai kungiyoyi da dama masu zaman kansu wato 'Non Governmental Organisations' NGO a takaice wanda suke a nan gida Arewa sunyi niyyar taimakawa wajen bada kula ga harkokin karatu  musamman na yara kanana da kuma marayu marasa galihu, shin ko ka shirya taimakon alu'ummmar ka? Ta wace hanya zaka iya bada gudunmuwarka domin cigaban Arewa? Wannan sune tambayoyi wanda ya kamata kayiwa kanka su.
Wata kungiyar matasa da naci karo da su ne yasa nayi wannan 'yar tunatarwar ga matasan mu na Arewa domin ganin yanda suka shirya tsaf dan tallafawa yaran Jahar Zamfara wurin karatun su.
A kasa zaka iya ganin su a cikin hoto. Ko da gani, ba sai an gaya maka ba lallai sun shirya tsaf dan ganin cewa yaran jahar su sun samu tallafi daga garesu. Shin ko kaima kana da niyyar taimakawa dan ganin an karfafawa ilimi a Arewa?

Wannan kungiyar matasan da na hadu da su a wata makaranta mai suna Ibrahim Gusau sun yiwa kansu suna da Juvenile Aid Foundation.

Wasu daga cikin Matasa 'yan kungiyar Juvenile Aid Foundation


Hakika wadannan matasa abun koyi ga sauran matasa da suke da karfi da kuma ikon tallafawa iyakar gwargwado domin ganin ilimi ya samu shiga a cikin dukkan wani kauye da ke Arewacin kasar nan.

A kasa zaku iya ganin yara 'yan makaranta da kuma sauran matsan nan na kungiyar Juvenile Aid Foundation.

Yara ;yan makaranta.
Idan ka duba daga kasa kuma, zaka ga shugaban Kungiyar yayin da yake mika kyauta ga wani dalibi.
Sugaban Kungiya yayin da yake mika kyauta ga wani dalibi.









Labels: ,

Monday, 16 October 2017

Yadda aure ke sauya mutane a tsawon rayuwa

"Wane dalili ne yasa ake da dimbim mata masu shekaru talatin da doriya basu da aure a kwanakin nan?"



A dakin taron walima na shirin kundin Bridget Jone wanda ya yi matukar sabo da kowane rukunin mutane da suka saba haduwa da su, a kebe, kewaye da abokai masu aure a daki guda.
Duk da cewa masana aikin kwakwalwa ba su samu cikakkiyar fahimtar da za ta tabbatar da cewa ko aure na sanya wa mutane natsuwa da gamsuwa.
Kamar kawayen Bridget ko kuma ana ingiza mutane ne kawai su ji suna son yin aure.
Bincike ya nuna cewa wadanda suka jajirce wajen haduwa don zaman rayuwa da wani mutum hakika suna samun sauyi da kimar mutuntaka a yanayin jin dadi da wahala.. har mai rabawa ta raba mu.
Al'amarin na da ma'ana baya ga cewa, nuna haduwar zaman tare da wani mutum a bainar jama'a na nuni da biyayya da hangen gaba.
Ba ma a yi la'akari daukacin sauyin tsarin rayuwa ga wasu, tabbas zaman tare na yau da kullum da mutum guda na matukar bukatar hakuri da masalahar zaman lumana.

Hattara ma'auratan da suka gamsu da juna: duk da cewa ana samun jin dadi na takaitacen lokaci ne, domin bayan an daura aure, cikin shekara guda sabani na iya sanyawa a sake lale.
Dangane da kowane irin sauyin kyautata rayuwa aure ke da tasirin haifarwa, abin tunani da alamar tambaya a kai shi bincike ya bai wa fifiko a daukacin fadin duniya, tun da miliyoyinmu na daura aure a kowace shekara.
A gaskiya, binciken da aka gudanar kan tambayar mamakinta ba shi da kima.
Ta yiwu mafi kyawun hujja ita ce wacce ta bayyana a nazarin baya-bayan nan da aka gudanar a kasar Jamus, inda masu binciken suka bi kadin sauyin mutuntakar al'umma kusan 15,000 a tsawon shekaru hudu.
An gano cewa marasa aure irin Bridget Jones da suka jajirce kan lamarin sun fi farin ciki.
Muhimmmin al'amari dai shi ne mutum 664 da aka bibiyi harkokinsu sun yi aure ne lokacin da suke karatu.
Inda aka kyale Jule Specht a Jami'ar Münster da abokan aikinta suka gano yadda kimar mutuntakarsu (halayyarsu) ta sauya in an kwatanta da sauran wadanda ba su da aure da aka bibiyi kadin lamarinsu.

Masu binciken sun gano cewa masu auren da aka yi binciken kansu an samu raguwar baza harkokin rayuwarsu a bainar jama'a in an kwatanta da sauran.
Bambancin da aka samu matsakaici ne, amma duk da haka ta yi wu ya bayar da hujja ingantacciya kan zargin da gwagware ke yi cewa abokansu masu aure ba sa shakatawa da holewa kamar yadda suke yi.
Duk da abin mamakin da a ke bazawa, ma'aurat ba kasafai suke suke daukar dabi'un (ha;layar) junansu a tsawon lokaci ba.
Tsarin nazarin ya tabbata ne musamman a kan mata, kamar yaddda yake kunshe a wani kwarya-kwaryar bincikee da aka gudanar a Amurka aka wallafa shi a shekarar 2000.
Inda masu binciken suka yi gwaji kan halayyar mutane fiye da 2000 masu matsakaitan shekaru da aka bibiyesu sau biyu tsawon shekaru shida zuwa tara.
A wancan lokacin, mata 20 masu aure, yayin da wasu 29 aka sake su.
Idan an yi kwatanceceniya tsakanin masu aure da wadanda aurensu ya rabu, wadanda suka samu rabuwar aure sun fi sakin jikinsu a bainar jama'a, kamar wadanda aka cire musu sasarin igiyar aure.
Sababbin ma'aurata maza kuwa, alamu na nuna sun yi matukar fa'idantuwa in an kwatanta da takwarorinsu wadanda suka samu rabuwar aure, inda suke nuna matukar halin kula da kwazo, sannan damuwarsu ta yi matukar raguwa.
Halin kula da ke bai wa maza masu aure kwarin gwiwa haka kawai yake bijirowa.
Duk mutumin da ke da aure (ko tarayyar masoya ta tsawon lokaci) zai san cewa akwai dimbin basirar da ake amfani da ita don tabbatar da dorewar auratayya wajen tarairayar harkokin gida masu tangal-tangal da jirrgin ruwan masu aure.
Wadannan su ne hakikanin al'amuran da aka gano sabuwar makalar da ka wallafa cikin wannan shekarar.

Maza masu aure sun fi nuna halin kula, kodayake a wasu lokutan sukan bar tufafinsu da suka yi dauda warwatse a daben daki.
Tawagar Jamusawan yamma masana aikin kwakwalwa, karkashin jagorancin Tila Pronk na Jami'ar Tilbug sun tabbatar da cewa mafi muhimmancin dabarar zamantakewar aure ko halayya shi ne iya tarairayar kai (yin dauriya da cijewa ta tsawon lokaci saboda aure) da yafiya.
Wato ta yadda za aka iya share abin da ya gabata na daga kuskure aboki/abokiyar zama a wani yanayi, wato kamar watsi da kayan sawa a kasa ko yabawa da nuna sha'awa makwafta.
Masu binciken sun dauki sababbin ma'aurata 199, inda suka auna kimar tasirin yafiya ga juna cikin watanni uku da aurensu wadanda aka bi Kadin lamarinsu an kiomanta amincewarsu da abubuwa kamar haka:
"Idan abokin zamana ya yi mini ba daidai ba, masalauha kawai in yafe kuma in manta" da yadda suke tarairayar kansu (wadanda aka bi kadin lamarinsu an kimanta aminceewarsu da al'amura kamar "Na iya kauce wa yaudarar daukar hankali").
Wadanda aka bibiyi lamarinsu an sake maimaita gwaje-gwajen a kansu kowace shekara har tsawon shekaru hudu.
Sakamakon binciken ya yi nuni da cewa wadanda aka bibiyi al'amauransu sun kara kaimin yafiya da tarairayar kansu tsawon lokacin da aka gudnar danazarin.
Kididdigar alkaluma ta nuna karuwar yafiya ta kasance tsaka-tsaki, yayin da karin iya tarairayar kai (kamun kai) ya zama kadan, amma Pronk da abokan aikinta sun yi nuni da cewa karuwar daidai take da ta kame kai da aka gano a mutanen da ke tsarin tunani musamman kokarin da aka yi wajen kama kai.
Masa aikin kwakwalwa ba su warware abin da ake son ganowa kan ko mutane na samun gamsuwar rayuwa da daina shan wuya idan sun yi aure.
Mene ne dalilin da ya sanya ma'aurata ke watsar da gamsuwar jin dadin rayuwa?
Muhimmiyar hujja ta bayyana a wasu nazarce-nazarce da aka gudanar kan gamsuwar rayuwa da sauye-sauyen samun farin ciki bayan aure.
Rukunin marasa aure irrin su Bridget Jones masu shekaru 30 da doriya za su yi murnar jin cewa duk da gamsuwar dadin rayuwa na karuwa bayan aure, aka kuma samu dalilin da zai haifar da koma-baya a sake lale bayan shekara guda.
Sai dai a iya cewa daukacin abin da aka gano ba lallai haka yake akan kowa ba.
Mun sha yin batu kan wasu mutane da ake kimanta su a matsayin miji nagari ko mata tagari (yayin da wasu sun fi son kasancewa a rayuwar gwagwarci), wannan mahangar madogara ce, domin hujja ta yi nuni kan yadda ma'aurata ke samun sauyin rayuwar farin ciki ya bambanta bisa la'akari da kimar mutunta ko halayyarsu kafin aure.
A wajen wasu, aure na samar da madawwamin farin ciki: musamman abin da ya shafi kula da kai da kunyar mata da sakin jikin maza da ke nuni da karin annashuwa da gamsuwar rayuwa in an yi aure, karara yake a bayyane saboda sababbin ma'aurata na da tsarin rayuwa da ya yi daidai da kimar mutuntakarsu (irin halayensu), duk da cewa dai har yanzu ba a yi nazarin al'amarin ba.

Mutanen da ke da aure ba su cika sakin jikinsu ko kai tsaye su yi ganganci aikata wani abu ba.
Karshen al'amuran, ko me za a ce kan abin da aka baza cewa ma'aurata kan dauki halayen junasu tsawon lokaci?
Akwai tabbaci kan haka in an yi la'akari da yadda tsofaffin ma'aurata ke sanya riga 'yar shara ko kayan motsa jiki szuna masu barkwanci.
Ta yiwu lamarin na da rikitarwar ban mamaki.
Idan haka kuwa, ana sa ran ma'auratan da suka dade da juna halayyarsu za ta yi daidai da ta abokan zamansu.
Sai dai masu bincike daga Jami'ar Jihar Michigan sun yi nazarin tantance halayyar ma'aurata fiye da 1,200, inda suka gano cewa alakar kadan ce ko ma babu ita sam kan wannan lamari.
Hakikanin gaskiya ita ce mutane da halayyarsu ta zamo iri guda sun fi auren juna karon farko.
Idan aka dauki al'amuran dungurrungum, binciken na nuni da cewa yana da matukar wuya a ce aure na sauya dabi'a.
Sai dai lamarin ba shi da alaka rudani da rikicin dan Adam da ka biyo baya, inda haihuwa 'ya'ya ke zuwa akai-akai.



Labels: